*HADUWAR SALLAR IDI DA SALLAR JUMA'A A ARANA GUDA* 2⃣
A rubutun baya idan ba'a manta ba mun kawo Aqwal din malamai akan mas'alar faduwar sallar juma'a akan duk wanda ya sallaci idi, awannan rubutu zamu bayyana dalilan kowane bangare in sha Allah Ta'ala.
📝 *DALILLAN JUMHUR*
jumhur na malamai sun tafi akan cewa wajibcin sallan juma'a baya faduwa akan mutum dan kawai ya halarci sallan idi, sun kafa hujja da Alqurani da kuma hadisi abisa wannan ra'ayi nasu, ga dalilan kamar haka;
🔹 *DALILINSU DAGA ALQURANI* fadin Allah subhanahu wa ta'ala
{إذا نودي للصلاة من يوم الجمعة فاسعوا إلى ذكر الله}.
Sukace acikin wannan Ayar Allah banbance tsakanin juma'ar da idi yazo acikinta ba da wacce baizo ba.
🔹 *DALILINSU DAGA ATHAR* fadin khalifa Uthman bin Affan Allah ya kara yarda dashi alokacin da yake khudbar sallan idi da ta fado aranar juma'a "Yaku mutane lalle awannan rana idi guda biyu sun hadu muku acikinta, duk wanda yakeso daga cikin wadanda suke kauyuka ya zauna ya jira sallan juma'a to ya jira, wanda kuma yakeso ya koma to na bashi izini".
Akarkashin wannan athar din malamai sun fitar da abubuwa kamar haka;
1. Khalifa uthman bin Affan Allah ya kara masa yarda ya kebance wadanda suke kauye ne kadai da zancen sa banda wanda suke cikin madina domin su wajibcin bai sauka akansu ba sabanin wadanda suke kauye su daman tun chan juma'a bata wajaba akansu ba.
2. Cewa da yayi duk wanda yakeso ya koma to na masa izini, yana magana akan wadanda zasu takura saboda nisansu ko kuma saboda zuwa su yanka abun yankarsu, ko wani abu makamancin haka.
🔹 *DALILINSU NA GABA* Sallar juma'a farilla ne bil ijma'i, amma ita sallar idi sunnah ce awurin jumhur na malamai, qa'ida kuma shine sunnah bata fadar da wajibi.
🔹 *DALILINSU NA GABA* kowacce daga cikin idi da juma'a sallace mai zaman kanta wata bata wakiltar wata kamar Sallar idi da sallar Azahar.
Wadannan sune dalilan jumhur da zamu takaitu akansu in sha Allah ta'ala arubutu na gaba zamu dora akan dalilan Hanabila.
Julaibeeb
08/12/1441
29/7/2020
#zaurenfisabilillah
https://t.me/Fisabilillaaah
A rubutun baya idan ba'a manta ba mun kawo Aqwal din malamai akan mas'alar faduwar sallar juma'a akan duk wanda ya sallaci idi, awannan rubutu zamu bayyana dalilan kowane bangare in sha Allah Ta'ala.
📝 *DALILLAN JUMHUR*
jumhur na malamai sun tafi akan cewa wajibcin sallan juma'a baya faduwa akan mutum dan kawai ya halarci sallan idi, sun kafa hujja da Alqurani da kuma hadisi abisa wannan ra'ayi nasu, ga dalilan kamar haka;
🔹 *DALILINSU DAGA ALQURANI* fadin Allah subhanahu wa ta'ala
{إذا نودي للصلاة من يوم الجمعة فاسعوا إلى ذكر الله}.
Sukace acikin wannan Ayar Allah banbance tsakanin juma'ar da idi yazo acikinta ba da wacce baizo ba.
🔹 *DALILINSU DAGA ATHAR* fadin khalifa Uthman bin Affan Allah ya kara yarda dashi alokacin da yake khudbar sallan idi da ta fado aranar juma'a "Yaku mutane lalle awannan rana idi guda biyu sun hadu muku acikinta, duk wanda yakeso daga cikin wadanda suke kauyuka ya zauna ya jira sallan juma'a to ya jira, wanda kuma yakeso ya koma to na bashi izini".
Akarkashin wannan athar din malamai sun fitar da abubuwa kamar haka;
1. Khalifa uthman bin Affan Allah ya kara masa yarda ya kebance wadanda suke kauye ne kadai da zancen sa banda wanda suke cikin madina domin su wajibcin bai sauka akansu ba sabanin wadanda suke kauye su daman tun chan juma'a bata wajaba akansu ba.
2. Cewa da yayi duk wanda yakeso ya koma to na masa izini, yana magana akan wadanda zasu takura saboda nisansu ko kuma saboda zuwa su yanka abun yankarsu, ko wani abu makamancin haka.
🔹 *DALILINSU NA GABA* Sallar juma'a farilla ne bil ijma'i, amma ita sallar idi sunnah ce awurin jumhur na malamai, qa'ida kuma shine sunnah bata fadar da wajibi.
🔹 *DALILINSU NA GABA* kowacce daga cikin idi da juma'a sallace mai zaman kanta wata bata wakiltar wata kamar Sallar idi da sallar Azahar.
Wadannan sune dalilan jumhur da zamu takaitu akansu in sha Allah ta'ala arubutu na gaba zamu dora akan dalilan Hanabila.
Julaibeeb
08/12/1441
29/7/2020
#zaurenfisabilillah
https://t.me/Fisabilillaaah
Telegram
FISABILILLAH 🌿
"Duk Wanda ya yi nuni akan aikin alkhairi, to, yana da lada kwatankwacin Wanda ya yi aikin"
https://www.facebook.com/Fisabilillaaah/
https://t.me/Fisabilillaaah
https://www.facebook.com/Fisabilillaaah/
https://t.me/Fisabilillaaah
❤2
*HADUWAR SALLAR IDI DA SALLAR JUMA'A A ARANA GUDA* 3⃣
A rubutu na biyu idan ba'a manta ba mun kawo dalilan jumhur akan rashin faduwar juma'a akan mutum dan ya halarci sallar idi, yanzu kuma zamu kawo dalilan Hanabila akan faduwar juma'a.
📝 *DALILAN HANABILA*
Hanibila sunyi istidlali da dalilai masu yawa amma zamu kawo kadan daga ciki in sha Allah,
🔹 *DALILINSU NA FARKO* Hadisin Ibnu Abi Ramla yake cewa Naga Mu'awiya bin Abi Sufyan yana tambaya Zaidu bin Arqam ko ya taba riskar manzon Allah alokacin da idi guda biyu suka hadu masa arana guda?? Sai zaidu yace eh, Sai Mu'awiya yace to ya manzon Allah yayi?? Sai Zaidu yace Manzon Allah ya sallaci idi Sannan yayi sauki gameda idi, kuma yace *"DUK WANDA YAKESON YA SALLACI JUMA'A TO YA SALLACE TA"*.
🔸 *DALILINSU NA BIYU* Hadisin Abi Huraira Allah ya kara masa yarda yace: Manzon Allah sallallahu alaihi wa sallama yace "Lalle awannan rana idi guda biyu sun hadu muku, duk wanda yaga dama idi ta isar masa daga juma'a amma mudai zamu hada duka biyu".
🔸 *DALILINSU NA UKU* sukace ai juma'a an banbanta ne kawai da Azahar saboda khudba wanda kuma an saurareta alokacin idi, hakan sai ya wadatar daga sake sauraronta a juma'a.
🔸 *DALILINSU NA HUDU* sukace "kuma ai lokacin sallan idi da juma'a lokaci dayane (kamar yadda yake awurin hanabila) Dan haka daya sai ta fadar da daya kamar juma'a da Azahar".
Wadannan sune wasu daga cikin dalilan da Hanabila sukayi istidlali dasu. Yanzu zamu leka dalilan ma'abota zance na uku masu cewa idan mutum yayi Sallar idi to babu wata sallah da zai sake sai la'asar, Juma'a da Azahar duk sun fadi akansa.
📝 *DALILIN MASU GANIN AZAHAR TA FADI AKAN WANDA YAYI IDI*
🔹 *DALILINSU* Shine hadisin Ada'u bin Abi Rabah Allah ya masa rahama yace "Abdullah bin Zubair ya mana sallah idi aranar juma'a afarkon yini, alokacin juma'a da muka zo domin sallatanta sai bai fito ba, sai kowa yayi Sallar sa shi kadai, alokacin kuma Abdullah bin Abbas ya da'ifa da yadawo sai muka labarta masa abunda ya faru sai Ibnu Abbas yace "Ya dace da sunnah".
Akarkashin wannan hadisin sukace, ai Abdullah bin Zubair bai fito wata sallah ba bayan sallan idi sai sallan la'asar, da aka labartawa Ibnu Abbas kuma sai ya tabbatar dashi akan haka har yake cewa ya dace da sunnah, wanda abune sananne aduk lokacin da Sahabi yace "ya dace da sunnah ko wani abu makamancin haka" to yana nufin Sunnar Annabi Muhammad sallallahu alaihi wa sallama.
Arubutu na gaba zamu bayyana abunda malamai suke rinjayarwa acikin wadannan zantuka guda ukun in sha Allah.
Julaibeeb
09/12/1441
30/7/2020
#zaurenfisabilillah
https://t.me/Fisabilillaaah
A rubutu na biyu idan ba'a manta ba mun kawo dalilan jumhur akan rashin faduwar juma'a akan mutum dan ya halarci sallar idi, yanzu kuma zamu kawo dalilan Hanabila akan faduwar juma'a.
📝 *DALILAN HANABILA*
Hanibila sunyi istidlali da dalilai masu yawa amma zamu kawo kadan daga ciki in sha Allah,
🔹 *DALILINSU NA FARKO* Hadisin Ibnu Abi Ramla yake cewa Naga Mu'awiya bin Abi Sufyan yana tambaya Zaidu bin Arqam ko ya taba riskar manzon Allah alokacin da idi guda biyu suka hadu masa arana guda?? Sai zaidu yace eh, Sai Mu'awiya yace to ya manzon Allah yayi?? Sai Zaidu yace Manzon Allah ya sallaci idi Sannan yayi sauki gameda idi, kuma yace *"DUK WANDA YAKESON YA SALLACI JUMA'A TO YA SALLACE TA"*.
🔸 *DALILINSU NA BIYU* Hadisin Abi Huraira Allah ya kara masa yarda yace: Manzon Allah sallallahu alaihi wa sallama yace "Lalle awannan rana idi guda biyu sun hadu muku, duk wanda yaga dama idi ta isar masa daga juma'a amma mudai zamu hada duka biyu".
🔸 *DALILINSU NA UKU* sukace ai juma'a an banbanta ne kawai da Azahar saboda khudba wanda kuma an saurareta alokacin idi, hakan sai ya wadatar daga sake sauraronta a juma'a.
🔸 *DALILINSU NA HUDU* sukace "kuma ai lokacin sallan idi da juma'a lokaci dayane (kamar yadda yake awurin hanabila) Dan haka daya sai ta fadar da daya kamar juma'a da Azahar".
Wadannan sune wasu daga cikin dalilan da Hanabila sukayi istidlali dasu. Yanzu zamu leka dalilan ma'abota zance na uku masu cewa idan mutum yayi Sallar idi to babu wata sallah da zai sake sai la'asar, Juma'a da Azahar duk sun fadi akansa.
📝 *DALILIN MASU GANIN AZAHAR TA FADI AKAN WANDA YAYI IDI*
🔹 *DALILINSU* Shine hadisin Ada'u bin Abi Rabah Allah ya masa rahama yace "Abdullah bin Zubair ya mana sallah idi aranar juma'a afarkon yini, alokacin juma'a da muka zo domin sallatanta sai bai fito ba, sai kowa yayi Sallar sa shi kadai, alokacin kuma Abdullah bin Abbas ya da'ifa da yadawo sai muka labarta masa abunda ya faru sai Ibnu Abbas yace "Ya dace da sunnah".
Akarkashin wannan hadisin sukace, ai Abdullah bin Zubair bai fito wata sallah ba bayan sallan idi sai sallan la'asar, da aka labartawa Ibnu Abbas kuma sai ya tabbatar dashi akan haka har yake cewa ya dace da sunnah, wanda abune sananne aduk lokacin da Sahabi yace "ya dace da sunnah ko wani abu makamancin haka" to yana nufin Sunnar Annabi Muhammad sallallahu alaihi wa sallama.
Arubutu na gaba zamu bayyana abunda malamai suke rinjayarwa acikin wadannan zantuka guda ukun in sha Allah.
Julaibeeb
09/12/1441
30/7/2020
#zaurenfisabilillah
https://t.me/Fisabilillaaah
Telegram
FISABILILLAH 🌿
"Duk Wanda ya yi nuni akan aikin alkhairi, to, yana da lada kwatankwacin Wanda ya yi aikin"
https://www.facebook.com/Fisabilillaaah/
https://t.me/Fisabilillaaah
https://www.facebook.com/Fisabilillaaah/
https://t.me/Fisabilillaaah
❤6
MA66UGAN FARIN CIKI
"Duk wanda bai samu farin ciki acikin zikirin Allah da sallah da karatun alqur'ani ba, to ba zai ta6a samun shi acikin wani abunda ba su ba." Inji Hasanul Basri (rahimahullah).
Ay "Da ambaton Allah zuqata suke samun natsuwa" kamar yadda yazo acikin Alqur'ani Mai girma.
#Zaurenfisabilillah
Telegram:
https://t.me/Fisabilillaaah
Instagram:
https://www.instagram.com/zaurenfisabilillah/
"Duk wanda bai samu farin ciki acikin zikirin Allah da sallah da karatun alqur'ani ba, to ba zai ta6a samun shi acikin wani abunda ba su ba." Inji Hasanul Basri (rahimahullah).
Ay "Da ambaton Allah zuqata suke samun natsuwa" kamar yadda yazo acikin Alqur'ani Mai girma.
#Zaurenfisabilillah
Telegram:
https://t.me/Fisabilillaaah
Instagram:
https://www.instagram.com/zaurenfisabilillah/
❤1
*GIDAUNIYAR NEMAN TAIMAKO NA NAMAN SALLAH GA MARAYU*
Mafi girman aiki da bawa zai yi wanda zai gadar masa da yardar Allah kuma ya bashi kusanci zuwaga Allah shine yayewa bayinsa damuwa da kuma sanya musu farin ciki.
Tabbas ladan aiki yana hauhawa a lokuta mafiya girma da daraja, daga cikin lokuta mafiya mafi girma kuwa akwai ranar babban sallah kamar yadda Sahabi Abdullahi bin Qarɗ Allah ya ƙara masa yarda yake cewa: Manzon Allah Sallallahu alaihi Wasallama yace "Mafi girman wuni awurin Allah shine ranar babban sallah (eidul adha) sai kuma washegarin ranar sallah ɗin)
صحيح أبي داود ١٧٦٥
Wannan zaure na fisabilillah ya haɗa gidauniya ta neman taimako domin sanyawa marayu farin ciki awannan rana mai girman daraja, ta hanyar samar musu abinda zasu ci da naman da zasu ɗan yi walwala dashi haɗe da suturar da zasu sanya awannan rana.
Kada ka raina abunda zaka bayar komin ƙanƙantarsa, zaka samu tagomashi mai girma awurin Allah.
*Domin taimakawa*
Acct No.: 0219529403
Account Name: ZAUREN FISABILILLAHI SERVICES
Bank: Union bank
*Domin neman ƙarin bayani*
08160287418
08137627053
07039397764
Allah ya bada ikon taimakawa.
#zaurenfisabilillah
https://t.me/Fisabilillaaah
Mafi girman aiki da bawa zai yi wanda zai gadar masa da yardar Allah kuma ya bashi kusanci zuwaga Allah shine yayewa bayinsa damuwa da kuma sanya musu farin ciki.
Tabbas ladan aiki yana hauhawa a lokuta mafiya girma da daraja, daga cikin lokuta mafiya mafi girma kuwa akwai ranar babban sallah kamar yadda Sahabi Abdullahi bin Qarɗ Allah ya ƙara masa yarda yake cewa: Manzon Allah Sallallahu alaihi Wasallama yace "Mafi girman wuni awurin Allah shine ranar babban sallah (eidul adha) sai kuma washegarin ranar sallah ɗin)
صحيح أبي داود ١٧٦٥
Wannan zaure na fisabilillah ya haɗa gidauniya ta neman taimako domin sanyawa marayu farin ciki awannan rana mai girman daraja, ta hanyar samar musu abinda zasu ci da naman da zasu ɗan yi walwala dashi haɗe da suturar da zasu sanya awannan rana.
Kada ka raina abunda zaka bayar komin ƙanƙantarsa, zaka samu tagomashi mai girma awurin Allah.
*Domin taimakawa*
Acct No.: 0219529403
Account Name: ZAUREN FISABILILLAHI SERVICES
Bank: Union bank
*Domin neman ƙarin bayani*
08160287418
08137627053
07039397764
Allah ya bada ikon taimakawa.
#zaurenfisabilillah
https://t.me/Fisabilillaaah
Telegram
FISABILILLAH 🌿
"Duk Wanda ya yi nuni akan aikin alkhairi, to, yana da lada kwatankwacin Wanda ya yi aikin"
https://www.facebook.com/Fisabilillaaah/
https://t.me/Fisabilillaaah
https://www.facebook.com/Fisabilillaaah/
https://t.me/Fisabilillaaah
❤6👎1
📌
Sahabi Thabit bn Dhahhak Allah ya ƙara yarda da shi yana cewa; Manzon Allah (SAW) ya ce: "Duk wanda ya kashe kansa da wani abu a duniya za'a masa azaba da wannan abun a ranar alƙiyama.
#Zaurenfisabilillah
Telegram:
https://t.me/Fisabilillaaah
Facebook:
https://www.facebook.com/Fisabilillaaah/
Sahabi Thabit bn Dhahhak Allah ya ƙara yarda da shi yana cewa; Manzon Allah (SAW) ya ce: "Duk wanda ya kashe kansa da wani abu a duniya za'a masa azaba da wannan abun a ranar alƙiyama.
#Zaurenfisabilillah
Telegram:
https://t.me/Fisabilillaaah
Facebook:
https://www.facebook.com/Fisabilillaaah/
❤3👍3
🪷MAFI ALHERI ACIKIN MUTANE🪷
Ibn Rajab (Rahimahullah) yana cewa: A takaice, mafi alheri acikin mutane shine;
❶ Wanda yafi amfanar da mutane
❷ Wanda yake yin hakuri da cutarwar mutane a gareshi.
Kamar yadda Allah Madaukaki Ya siffanta salihai acikin fadinSa:
*"Waɗanda suke ciyarwa acikin sauƙi da tsanani kuma suke masu haɗiyewar fushi, kuma masu yafe wa mutane laifi. Kuma Allah Yana son masu kyautatawa."*
[Ali Imran : 134]
📚 لطائف المعارف ( ص 231 )
#Zaurenfisabilillah
Telegram:
https://t.me/Fisabilillaaah
Instagram:
https://www.instagram.com/zaurenfisabilillah/
Ibn Rajab (Rahimahullah) yana cewa: A takaice, mafi alheri acikin mutane shine;
❶ Wanda yafi amfanar da mutane
❷ Wanda yake yin hakuri da cutarwar mutane a gareshi.
Kamar yadda Allah Madaukaki Ya siffanta salihai acikin fadinSa:
*"Waɗanda suke ciyarwa acikin sauƙi da tsanani kuma suke masu haɗiyewar fushi, kuma masu yafe wa mutane laifi. Kuma Allah Yana son masu kyautatawa."*
[Ali Imran : 134]
📚 لطائف المعارف ( ص 231 )
#Zaurenfisabilillah
Telegram:
https://t.me/Fisabilillaaah
Instagram:
https://www.instagram.com/zaurenfisabilillah/
❤3👍1
*MUNA DAF DA SHIGA KWANAKI GOMAN FARKO NA ZUL-HIJJA IN SHAA ALLAHU*
Manzon Allah (SAW) ya ce; "Babu wasu ranaku da aikata wani aiki mai kyau ya fi soyuwa a wurin Allah sama da wadannan kwanaki goman, sai sahabbai suka ce ya Manzon Allah har jihadi bai kai su ba?? Sai manzon Allah ya ce eh har jihadi bai kai su ba, sai dai kadai mutumin da ya fita shi da dukiyarsa sannan ba abunda ya dawo daga cikinsu (dukiyar ta kare shima an kasheshi a filin yaƙi) -Sahih Tirmizi
#Zaurenfisabilillah
TELEGRAM:
https://t.me/Fisabilillaaah
FACEBOOK:
https://www.facebook.com/Fisabilillaaah/
Manzon Allah (SAW) ya ce; "Babu wasu ranaku da aikata wani aiki mai kyau ya fi soyuwa a wurin Allah sama da wadannan kwanaki goman, sai sahabbai suka ce ya Manzon Allah har jihadi bai kai su ba?? Sai manzon Allah ya ce eh har jihadi bai kai su ba, sai dai kadai mutumin da ya fita shi da dukiyarsa sannan ba abunda ya dawo daga cikinsu (dukiyar ta kare shima an kasheshi a filin yaƙi) -Sahih Tirmizi
#Zaurenfisabilillah
TELEGRAM:
https://t.me/Fisabilillaaah
FACEBOOK:
https://www.facebook.com/Fisabilillaaah/
❤4👍1
MUN SHIGA WATAN DHUL HIJJAH
💧 Mun shiga watan Zhul hijja, kada ku yi sakaci a cikin kwanaki goman farkon nan, ta yiwu wasu alkhairi masu yawa sun wuce ka a Ramadhan to ga dama ta samu, kwana goma ne ba yawa, se dai ayyuka alkhairi suna da girma wurin Allah.
🌹An karbo daga Abdullahi ɗan Abbas Allah ya yarda dashi yana cewa Manzon Allah yace "Babu wani aiki wanda yafi tsarkaka a wajen Allah sannan kuma yake da girman lada fiye da aikin da aka yishi acikin kwanakin goman layya" sai akace masa harda jihadi? sai yace eh! harda jihadi sai dai wanda ya fita da dukiyarsa,sannan babu wanda ya dawo acikinsu"سنن الدارمي ٢/١٧٧٤
💧Mu dage da ayyuka alkhairi kada mu yi sakaci da damar mu, Mu yawaita karanta Al_K'ur'ani da sauran nau'ikan Zikiri, Azumi, Sadaka, tausaya masu rauni, Nafiloli (Sallan dare) sada zumunta da dukiya, da kuma ziyara, watsa alkhairi da ilmi tsakanin mutane da yawaita kabbarori.
Allah Ta'ala yasa mu dace.
#Zaurenfisabilillah
TELEGRAM:
https://t.me/Fisabilillaaah
💧 Mun shiga watan Zhul hijja, kada ku yi sakaci a cikin kwanaki goman farkon nan, ta yiwu wasu alkhairi masu yawa sun wuce ka a Ramadhan to ga dama ta samu, kwana goma ne ba yawa, se dai ayyuka alkhairi suna da girma wurin Allah.
🌹An karbo daga Abdullahi ɗan Abbas Allah ya yarda dashi yana cewa Manzon Allah yace "Babu wani aiki wanda yafi tsarkaka a wajen Allah sannan kuma yake da girman lada fiye da aikin da aka yishi acikin kwanakin goman layya" sai akace masa harda jihadi? sai yace eh! harda jihadi sai dai wanda ya fita da dukiyarsa,sannan babu wanda ya dawo acikinsu"سنن الدارمي ٢/١٧٧٤
💧Mu dage da ayyuka alkhairi kada mu yi sakaci da damar mu, Mu yawaita karanta Al_K'ur'ani da sauran nau'ikan Zikiri, Azumi, Sadaka, tausaya masu rauni, Nafiloli (Sallan dare) sada zumunta da dukiya, da kuma ziyara, watsa alkhairi da ilmi tsakanin mutane da yawaita kabbarori.
Allah Ta'ala yasa mu dace.
#Zaurenfisabilillah
TELEGRAM:
https://t.me/Fisabilillaaah
❤5👍2
AZUMIN RANAR ARAFAH
Manzon Allah SAW ya ce; "Azumin ranar arfa ina tsammanin Allah zai gafarta zunuban shekarar bayansa da shekarar gabansa". - (Muslim)
Allah Ta'ala ya bamu iko yi.
#Zaurenfisabilillah
Telegram:
https://t.me/Fisabilillaaah
Facebook:
https://www.facebook.com/Fisabilillaaah/
Manzon Allah SAW ya ce; "Azumin ranar arfa ina tsammanin Allah zai gafarta zunuban shekarar bayansa da shekarar gabansa". - (Muslim)
Allah Ta'ala ya bamu iko yi.
#Zaurenfisabilillah
Telegram:
https://t.me/Fisabilillaaah
Facebook:
https://www.facebook.com/Fisabilillaaah/
👍1👏1
Forwarded from FISABILILLAH 🌿
*MAFI ALKHAIRIN ADDUA, ADDUAR RANAR ARAFA*💧
Manzon Allah (SAW) ya ce, "Mafi alkhairin addua'a ita ce Adduar ranar Arfa, mafi alkhairin abinda na fada ni da Annabawan da suke kafi na shine; LA'ILAHA ILLALLAHU WAHDAHU LAA SHARIKA LAHU, LAHUL MULKU WA LAHUL HAMDU WA HUWA ALA KULLI SHAI'IN K'ADIR. - Tirmizi
#ranar Arafa, mu yawaita addua da tuba da neman gafara, da sauran ibadoji, rana ce ta ƴanta bayi da kuma rabon Aljannah. Matsayin wannan rana kamar matsayin Lailatul ƙadri ne a cikin darare. Mu dage da addu'a da ibada, A yi ta wannan addua, a hanya ne ko a gida ko kasuwa.
#Zaurenfisabilillah
Telegram:
https://t.me/Fisabilillaaah
Facebook:
https://www.facebook.com/Fisabilillaaah/
Manzon Allah (SAW) ya ce, "Mafi alkhairin addua'a ita ce Adduar ranar Arfa, mafi alkhairin abinda na fada ni da Annabawan da suke kafi na shine; LA'ILAHA ILLALLAHU WAHDAHU LAA SHARIKA LAHU, LAHUL MULKU WA LAHUL HAMDU WA HUWA ALA KULLI SHAI'IN K'ADIR. - Tirmizi
#ranar Arafa, mu yawaita addua da tuba da neman gafara, da sauran ibadoji, rana ce ta ƴanta bayi da kuma rabon Aljannah. Matsayin wannan rana kamar matsayin Lailatul ƙadri ne a cikin darare. Mu dage da addu'a da ibada, A yi ta wannan addua, a hanya ne ko a gida ko kasuwa.
#Zaurenfisabilillah
Telegram:
https://t.me/Fisabilillaaah
Facebook:
https://www.facebook.com/Fisabilillaaah/
❤2🙏2
ZUCIYA DA LOKACI
Ya kamata mutum ya sani cewa abubuwa biyun nan sune mafiya daraja: zuciyarsa da lokacinsa. Idan yayi sakaci da lokacinsa kuma ya lalatar da zuciyarsa fa'idar rayuwarsa zata gushe.
حفظ العمر لابن الجوزي
#Zaurenfisabilillah
Telegram:
https://t.me/Fisabilillaaah
Instagram:
https://www.instagram.com/zaurenfisabilillah/
Ya kamata mutum ya sani cewa abubuwa biyun nan sune mafiya daraja: zuciyarsa da lokacinsa. Idan yayi sakaci da lokacinsa kuma ya lalatar da zuciyarsa fa'idar rayuwarsa zata gushe.
حفظ العمر لابن الجوزي
#Zaurenfisabilillah
Telegram:
https://t.me/Fisabilillaaah
Instagram:
https://www.instagram.com/zaurenfisabilillah/
👍4❤3👏1
Forwarded from FISABILILLAH 🌿
WANE TANADI KA YI MA KANKA GAME DA SADAKA MAI GUDANA??
💧Sahabi Abi Huraira ya ruwaito hadisi daga Manzon (SAW) yana cewa: "Lallai yana daga cikin abinda yake riskar mumini na aikin sa da ladarshi bayan mutuwar shi;
● Wani ilmi da ya koyar da shi, kuma ya yaɗa shi.
● Da Ɗa nagari da ya bari.
● Da kuma wani Alqur'ani da ya gadar da shi.
● Ko kuma wani masallaci daya gina.
● Ko wani gida ga matafiya da ya gina shi.
● Ko wata ƙorama da janyo.
● Ko wata Sadaqa da ya fitar da ita daga cikin dukiyarsa, a lokacin lafiyar shi, a halin rayuwar shi.
To, wannan duka zasu riske shi a bayan rayuwar shi.
Ibn Majah, kuma Al-baniy ya ingantashi. Duba (Dariqus salihin)
Note:
• Sadaqa mai gudana (Sadaqatu Jariya) shine duk wani aiki da ladan sa bazai yanke maka ba har bayan ka mutu.
• Malamai suka ce fadin Manzon Allah (SAW) "ko wani ɗa na gari" . Ai idan ka dace da ɗa nagari da yake aikata alkhairi zaka rika samun lada.
• "Ko wani Alƙur'ani da ya gadar" ma'ana, ya rubuta wani mus'hafi na Alqur'ani ya barshi ake karantawa, ko ya saya ya bayar, ko mutum ya bar nashi aka dauka ake karantawa. Zai rika samun lada.
Allah Ta'ala ka azurtamu da ayyukan alkhairi da zamu riƙa samun ladan su bayan rayuwar mu.
#Zaurenfisabilillah
https://whatsapp.com/channel/0029Va54zoM2f3EGKKcyG33Z
💧Sahabi Abi Huraira ya ruwaito hadisi daga Manzon (SAW) yana cewa: "Lallai yana daga cikin abinda yake riskar mumini na aikin sa da ladarshi bayan mutuwar shi;
● Wani ilmi da ya koyar da shi, kuma ya yaɗa shi.
● Da Ɗa nagari da ya bari.
● Da kuma wani Alqur'ani da ya gadar da shi.
● Ko kuma wani masallaci daya gina.
● Ko wani gida ga matafiya da ya gina shi.
● Ko wata ƙorama da janyo.
● Ko wata Sadaqa da ya fitar da ita daga cikin dukiyarsa, a lokacin lafiyar shi, a halin rayuwar shi.
To, wannan duka zasu riske shi a bayan rayuwar shi.
Ibn Majah, kuma Al-baniy ya ingantashi. Duba (Dariqus salihin)
Note:
• Sadaqa mai gudana (Sadaqatu Jariya) shine duk wani aiki da ladan sa bazai yanke maka ba har bayan ka mutu.
• Malamai suka ce fadin Manzon Allah (SAW) "ko wani ɗa na gari" . Ai idan ka dace da ɗa nagari da yake aikata alkhairi zaka rika samun lada.
• "Ko wani Alƙur'ani da ya gadar" ma'ana, ya rubuta wani mus'hafi na Alqur'ani ya barshi ake karantawa, ko ya saya ya bayar, ko mutum ya bar nashi aka dauka ake karantawa. Zai rika samun lada.
Allah Ta'ala ka azurtamu da ayyukan alkhairi da zamu riƙa samun ladan su bayan rayuwar mu.
#Zaurenfisabilillah
https://whatsapp.com/channel/0029Va54zoM2f3EGKKcyG33Z
❤3
WATAN ALLAH MUHARRAM
Ibnu Rajab Allah ya masa rahama yana cewa; "Haƙiƙa Annabi Muhammad (SAW) ya ambaci watan Al-Muharram da watar Allah, saboda girmanta da falalarta, domin Allah baya jingina wani abu gareshi sai abunda yake da daraja acikin halittunsa, kamar yadda ya jingina Annabi Muhammad da Annabi Ibrahim da Annabi Ishaq da Annabi Yaqub da sauran Annabawa zuwa ga bautarsa".
لطائف المعارف
💧MUHARRAM yana cikin watanni hudu masu alfarma, Imamul Qurdibi R. Yace: "Allah ya keɓance watanni huɗu masu alfarma ne da ambato da kuma Hani da yin zalunci a cikin su, saboda girman sha'anin su duk da cewa zalunci haramunne a kowane lokaci.
💧Jamhur din malamai da imamai guda uku Abu Hanifa, Malik da Shafi'i duk sun tafi akan mustahabbine (anso) mutum ya yawaita azumi acikin su waɗannan watanni guda hudu, ya kuma ƙara kaimi a cikin musamman MUHARRAM da Rajab.
#Zaurenfisabilillah
28/12/1441
18/8/2020
Telegram: https://t.me/Fisabilillaaah
Ibnu Rajab Allah ya masa rahama yana cewa; "Haƙiƙa Annabi Muhammad (SAW) ya ambaci watan Al-Muharram da watar Allah, saboda girmanta da falalarta, domin Allah baya jingina wani abu gareshi sai abunda yake da daraja acikin halittunsa, kamar yadda ya jingina Annabi Muhammad da Annabi Ibrahim da Annabi Ishaq da Annabi Yaqub da sauran Annabawa zuwa ga bautarsa".
لطائف المعارف
💧MUHARRAM yana cikin watanni hudu masu alfarma, Imamul Qurdibi R. Yace: "Allah ya keɓance watanni huɗu masu alfarma ne da ambato da kuma Hani da yin zalunci a cikin su, saboda girman sha'anin su duk da cewa zalunci haramunne a kowane lokaci.
💧Jamhur din malamai da imamai guda uku Abu Hanifa, Malik da Shafi'i duk sun tafi akan mustahabbine (anso) mutum ya yawaita azumi acikin su waɗannan watanni guda hudu, ya kuma ƙara kaimi a cikin musamman MUHARRAM da Rajab.
#Zaurenfisabilillah
28/12/1441
18/8/2020
Telegram: https://t.me/Fisabilillaaah
❤12
Forwarded from FISABILILLAH 🌿
AZUMIN TASU'A DA ASHURA
TASU'A: Shi ne Azumin ranar Tara ga watan Muharram, an shar'anta shi ne dan saɓawa Yahudawa, Manzon Allãh (SAW) yana cewa, Idan Allah ya rayani zuwa shekara mai zuwa zan azumci ranan tara ga wata. - Muslim (1134)
ASHURA: Manzon Allah (SAW) Ya ce game da Azumin ranan goma ga watan Muharram (Ashura) ina kyautata tsammanin a wurin Allah da ya kankare zunuban shekarar da ta gabace shi. - Muslim (1162).
Allah Ta'ala ya bamu ikon Azumta
#Zaurenfisabilillah
Telegram: https://t.me/Fisabilillaaah
TASU'A: Shi ne Azumin ranar Tara ga watan Muharram, an shar'anta shi ne dan saɓawa Yahudawa, Manzon Allãh (SAW) yana cewa, Idan Allah ya rayani zuwa shekara mai zuwa zan azumci ranan tara ga wata. - Muslim (1134)
ASHURA: Manzon Allah (SAW) Ya ce game da Azumin ranan goma ga watan Muharram (Ashura) ina kyautata tsammanin a wurin Allah da ya kankare zunuban shekarar da ta gabace shi. - Muslim (1162).
Allah Ta'ala ya bamu ikon Azumta
#Zaurenfisabilillah
Telegram: https://t.me/Fisabilillaaah
Forwarded from FISABILILLAH 🌿
KA GAMSU DA RABON DA ALLAH YA BAKA
Hasanul-Baṣri (Allah ya yi masa rahama) yana cewa:
"Duk wanda ya gamsu da rabon da Allah Ya raba Ya bashi, toh Allah zai wadatar masa kuma zai albarkace shi (acikinsa), amma wanda bai gamsu (da abunda Allah Ya raba Ya bashi ba), to Allah ba zai wadatar da shi acikin sa ba kuma ba zai sami albarkarsa ba."
[Kitabul-Riḍā ʿan Allāh bi Qaḍāʾihi 95]
#Zaurenfisabilillah
Telegram:
https://t.me/Fisabilillaaah
Instagram:
https://www.instagram.com/zaurenfisabilillah/
Hasanul-Baṣri (Allah ya yi masa rahama) yana cewa:
"Duk wanda ya gamsu da rabon da Allah Ya raba Ya bashi, toh Allah zai wadatar masa kuma zai albarkace shi (acikinsa), amma wanda bai gamsu (da abunda Allah Ya raba Ya bashi ba), to Allah ba zai wadatar da shi acikin sa ba kuma ba zai sami albarkarsa ba."
[Kitabul-Riḍā ʿan Allāh bi Qaḍāʾihi 95]
#Zaurenfisabilillah
Telegram:
https://t.me/Fisabilillaaah
Instagram:
https://www.instagram.com/zaurenfisabilillah/
❤7
KADA KA YANKE ƘAUNA DAGA RAHAMAR ALLAH
💧Ibnul Jauzi Allah ya masa rahama yana cewa; "Kada ka yarda kana ganin tsayin lokacin bala'i har takai ka gajiya da yawan addu'a, domin kai an jarrabeka da wannan bala'inne, sai kuma aka bautar dakai da hakuri, dan haka kada ka yanke kauna daga rahamar Allah koda kuwa bala'in ya jima"
...صيد الخاطر ص439
#Zaurenfisabilillah
TELEGRAM: https://t.me/Fisabilillaaah
💧Ibnul Jauzi Allah ya masa rahama yana cewa; "Kada ka yarda kana ganin tsayin lokacin bala'i har takai ka gajiya da yawan addu'a, domin kai an jarrabeka da wannan bala'inne, sai kuma aka bautar dakai da hakuri, dan haka kada ka yanke kauna daga rahamar Allah koda kuwa bala'in ya jima"
...صيد الخاطر ص439
#Zaurenfisabilillah
TELEGRAM: https://t.me/Fisabilillaaah
❤6
🥀🥀___
Ibnul-Qayyim (R) ya ruwaito daga Jariri cewa:
“An bani labarin wani mutum daga Banu Isra’ila wanda yake da wata bukata da yake so Allah ya biya masa. Don haka, sai ya shagaltu acikin yin ibada sannan kuma yana mai rokon Allah Ya biya masa bukatarsa. Lokacin da bai ga cewa bukatarsa ta biya ba, sai ya kwana yana zargin kansa, yana cewa: “Ya kai! Me ke damunka wanda yake hana a biya maka bukatunka? ” (wato yana tambayar kansa kenan)
Sai ya kwana acikin bakin ciki yana mai tuhumar kansa, yana cewa: "Tallahi, matsalar ba ta kasance daga Ubangijina ba. Hakika dalilin rashin samun biyan wannan bukatar tawa tana tattare dani.," kuma ya kasance cikin irin wannan halin na ɗora wa kansa alhakin (rashin samun biyar bukatar) har sai da a ƙarshe ya samu biyan buƙatarsa."
📖Ighasatul-Lahfan' (1/77)
'Yan uwa mu dage da yawan tuba da komawa ga Allah. Sau da dama silar rashin samun biyan bukatun mu suna tattare damu.
#Zaurenfisabilillah
Telegram: https://t.me/Fisabilillaaah
Ibnul-Qayyim (R) ya ruwaito daga Jariri cewa:
“An bani labarin wani mutum daga Banu Isra’ila wanda yake da wata bukata da yake so Allah ya biya masa. Don haka, sai ya shagaltu acikin yin ibada sannan kuma yana mai rokon Allah Ya biya masa bukatarsa. Lokacin da bai ga cewa bukatarsa ta biya ba, sai ya kwana yana zargin kansa, yana cewa: “Ya kai! Me ke damunka wanda yake hana a biya maka bukatunka? ” (wato yana tambayar kansa kenan)
Sai ya kwana acikin bakin ciki yana mai tuhumar kansa, yana cewa: "Tallahi, matsalar ba ta kasance daga Ubangijina ba. Hakika dalilin rashin samun biyan wannan bukatar tawa tana tattare dani.," kuma ya kasance cikin irin wannan halin na ɗora wa kansa alhakin (rashin samun biyar bukatar) har sai da a ƙarshe ya samu biyan buƙatarsa."
📖Ighasatul-Lahfan' (1/77)
'Yan uwa mu dage da yawan tuba da komawa ga Allah. Sau da dama silar rashin samun biyan bukatun mu suna tattare damu.
#Zaurenfisabilillah
Telegram: https://t.me/Fisabilillaaah
*A QONASHI*
Sheikh Uthaymeen (R) yana cewa: “Ina nasiha ga ‘yan uwana masu jefar da takarda, da su dinga dubawa kafin su jefar. Idan suka ga aya ko hadisi daga Manzon Allah (ﷺ) ajiki toh su qona kada su jefar. Kuma su dinga kulawa sosai kada suyi sakaci da hakan."
فتاوى نور على الدرب (٢/٥)
#Zaurenfisabilillah
Telegram:
https://t.me/Fisabilillaaah
Instagram:
https://www.instagram.com/zaurenfisabilillah/
Sheikh Uthaymeen (R) yana cewa: “Ina nasiha ga ‘yan uwana masu jefar da takarda, da su dinga dubawa kafin su jefar. Idan suka ga aya ko hadisi daga Manzon Allah (ﷺ) ajiki toh su qona kada su jefar. Kuma su dinga kulawa sosai kada suyi sakaci da hakan."
فتاوى نور على الدرب (٢/٥)
#Zaurenfisabilillah
Telegram:
https://t.me/Fisabilillaaah
Instagram:
https://www.instagram.com/zaurenfisabilillah/
👏2