Aihausanovels
185 subscribers
54 links
Domin samun Cikakkun Littattafan Hausa, yaΖ™i, almara da dai sauransu
Download Telegram
Channel photo updated
MAZA GUDU
Littafi na Biyar (5)
Complete book 5
Na abdul aziz sani..
Ita kuwa mahaifiyata rugowa tayi da gudu ta rungumeni kuma ta fashe da kukan farin ciki. Bayan an bani kambun Sarauta na gasa, wato mahaifina da kansa ya kwance kambun daga jikin hannunsa ya daura a nawa, sai mutane suka rude da kabbara aka cigaba dayi mini jinjina, a lokacin ne mahaifina ya daga kansa da hannayensa sama yayiwa Allah
godiya cikin matukar farin ciki daya sanya dansa ya gajeshi. Kwatsam a na cikin wannan dimbin farinciki ne aka hango wani mahayi ya durfafo cikin garin a guje bisa wani ingarman doki, tun daga nesa aka gane cewa bako ne kuma yana sanye da tufafi irin na dakarun birnin Kisra.
Da isowar wannan badakare daf da sarkinmu sai ya tsayar da dokinsa ya sauko kasa da sauri ya zube a gaban sarki ya kwashi gaisuwa, sannan yace, ya shugabana, Sarki Zaldasi Bin Auzir na birnin Kisra ya aiko ni gareka da wasika, ni manzo ne daga gareshi don haka ina jiran amsar da zan maida masa...

Domin jin yadda zata kaya sai ku taΙ“a hoton dake Ζ™asa don sauke Complete Ι—in littafin a wayoyinsu.
πŸ‘‡πŸ‘‡πŸ‘‡πŸ‘‡πŸ‘‡πŸ‘‡
https://www.aihausanovels.com.ng/2021/08/sa-maza-gudu-littafi-na-5-advanture.html
KaunarMu Complete Document
Na Mamuhgee

Gyara zamanta tayi akan kujerar dake fuskantar ta Dr Fatima Omar yonas tareda gyara zaman glasses na idonta ta bude bakinta dake mata nauyi aduk lokacinda zatayi maganar 'yar uwarta sbd jin kunyar kanta da takaicin kanta akan yanda konyaushe 'yar uwartace ciwon ranta da damuwarta,

Duk yanda taso dauke Kai da danne alamarin ako yaushe sabo abin ke dawo mata sbd tsoron meyene zata samu agaba 'yar uwarta ta rabata dashi sbd wannan shine asalin dumuwarta da tsoronta sbd batasan mezata iya zama agaba ba itama akan hakan.

Kamar yanda tasaba kullum idan tazo gurin Dr Fatima yonas yauma farawa tayi da cewa"

Sunana AYSHAT HAMEEDA NUHU MANDE sunan Tawainiyar haihuwata KHADIJA MUFEEDA NUHU MANDE,
yan biyu mahaifiyarmu ta haifemu shekara ashirin dasuka wuce,
Mintuna biyarne kacal atsakanin haihuwar tamu,
Nice nafara fitowa duniyar kafin ita,
Nice na cancanci mafi yawan soyayya da qauna daga iyayenmu da danginmu kafin ita sbd nice nafara haskaka idanuwansu dasuka jima da jiran ganin wannan Rana dazasu rungumi nasu 'yayan suma kasancewar sun jima harsun fara manyanta babu haihuwa,

Bayan fitowata duniya iyayena sunyi farin ciki mara misali na samuwata Saidai SO da QAUNA Dana samu daga garesu na mintuna biyarne kacal sbd fitowar 'yar uwata duniya ya sauyamin komai har zuwa yanzu,

Itace sanyin idanuwansu,
Itace farin cikin gidansu da wajensu,
Saidai Allah dayafisu iko da ita bai sakota a duniyarba sai daukeda cuta ta *_RAUNIN ZUCIYA_* ma'ana _*WEAK HEART*_ _*(CARDIOMYOPATHY)*_

Wannan cuta datake daukeda ita ta qara rage kaifin qauna dake tsakanina da iyayenmu,yan uwanmu,likitocin da duniyama gabaki daya.,

Ciwon raunin zuciyarta yasa ba'a qaunar bacin ranta,baa mata fada,baa ganin laifinta,kowa qaunarta yakeyi,kowa sonta yakeyi Wanda tuni gata yayi mata yawa tako wane bangare musamman Kai tsaye mahaifiyar dadynmu ta yanke cewa asakawa 'yar uwata sunanta tanason ta gajeta
Ba 6ata lokaci taci sunan kakarmu da mahaifiyarmu wato KHADIJA MUFEEDA inda ni naci sunan Mahaifiyar mamanmu wato AYSHAT HAMEEDA.
Domin sauke littafin a wayarku ta hannu sai ku danna hoton dake Ζ™asa.
πŸ‘‡πŸ‘‡πŸ‘‡πŸ‘‡
https://www.aihausanovels.com.ng/2021/08/kaunar-mu-complete-hausa-novel-document.html
ADANDI - Hausa Novel Document
Fauziyya Tasi'u Umar
Da mugun gudu motar me qirar Ferrari ta shigo makarantar Adon Bayero University wadda suke Kira da new set birki ta taka da sauri tare da furta β€œya Salam na bigeshi wlh na bigeshi rahama" tana fadin haka ta balle murfin motar ta fito da sauri wata kyakkyawar budurwa ce chocolate color wadda da gani babu tambaya kasan tanaji da kanta kuma tana tashen rashin kunya duba da yanayin shigarta.




Riga da wando ne farin jeans da jar riga three quarter ta hade gashinta na fulanin asali ta daure a baya ta dora wata hula me kamar nadin gammo a kanta tsakiyar kanta a waje ta zuba zobunan gold qafa da hanu sai daukar ido takeyi kamar walqiya duk wani lafiyayyen namiji idan yaganta a yanda take sai yaji yarr a jikinsa yanda take takawa duwaiwakanta na juyawa hips dinta yana daukan hankalin maza duk inda kyau yake Samha takai a kirata kyakkyawa.




Da dan sassarfarta ta qarasa ta tsuguna gaban kyakkyawan farin saurayin takai hanunta zata kamoshi ya kuwa daga hanu ya dauketa da wani lafiyayyen mari ta dafe gurin da sauri ta dago ta dubeshi bakinta yana rawa kafin tayi mgn ya sake dauketa da mari yace β€œke wacce irin yar iska ce ki rinqa yiwa makaranta shigar isa saboda rashin tarbiyya dubeki waike kin waye jahila daqiqiya dake saboda kunfi qarfin kowa shiya aka kyaleku kuke abinda kukeso to wlh ba commusioner ko gwamna ne ubanki zan iya bi dake da abinda kike taqama dashi banza shashasha ballagaza kawai dubi shigarki waike qaramar yar iska mtssss"
Domin Sauke Cikakken Littafin nan a ciki wayarku ta hannu sai ku danna hoton dake Ζ™asa ko kuma bulun rubutun dake kasa.
πŸ‘‡πŸ‘‡πŸ‘‡πŸ‘‡πŸ‘‡
https://www.aihausanovels.com.ng/2021/09/adandi-latest-hausa-novel-ummu-haira.html
Share it πŸ‘
*Rikici ya barke tsakanin Jamila Makira da mashiryin shirin |*

Ƙarin Bayani πŸ‘‡πŸ‘‡πŸ‘‡
https://www.aihausanovels.com.ng/2021/10/rikici-ya-barke-tsakanin-jamila-makira.html
.
Bakin Ciki Episode 1 Latest Hausa Novel Audio.

Ku danna bulun rubutun dake Ζ™asa ko kuma hoton domin sauraron Labarin.

πŸ‘‡πŸ‘‡πŸ‘‡πŸ‘‡

https://youtu.be/ZoZTiSAO2h0
Please Share πŸ‘
Bakin Ciki Episode 2 Latest Hausa Novel Audio.

Ku danna bulun rubutun dake Ζ™asa ko kuma hoton domin sauraron Labarin.

πŸ‘‡πŸ‘‡πŸ‘‡πŸ‘‡

https://youtu.be/lUpslqR0G8E
Please Share πŸ‘
Matar Makaho - Hausa Novel Document

Kuka nake baji ba gani bakin ciki ke dankare a cikin zuciya ta Wanda in har banyi kuka ba bazanji saukin suba Wai ni ce amarya amaryan ma na makaho mara ido na daga lulubena kasanciwar dakin akwai wutan nepa glop ya haska Koh ido shiya bani Daman ganin daki dakin da Koh a mafarki van taba tunanin akwai ranan da Zan iyya rayuwa a irin Shiba Wai yau shi ake Kira da dakina na aure ni sumayya bansan lokacin da wani irin kuka ya sarkeni ba cikin takaici Mai tarin yawa ya Allah me naiwa Yan uwan mahaifina da suka sakamin da wannan rayuwa Mai na tsare...

Domin sauke cikakken littafin sai ku danna bulun rubutun dake Ζ™asa ko kuma hoton.

πŸ‘‡πŸ‘‡πŸ‘‡πŸ‘‡

https://www.aihausanovels.com.ng/2021/10/matar-makaho-complete-hausa-novel.html

.
*Yadda Zaku Duba Sakamakon Jarabawarku Ta Nemi. A Wayoyin Hannunku |*

https://www.aihausanovels.com.ng/2021/10/yadda-zaku-duba-sakamakon-jarabawarku.html


Please share it
*Hadi Daga Allah Complete Hausa Novel Document |*

Wani tangamemen gida na hango mai girman gaske, gida ne Wanda ya amsa sunan sa gida, _na bude get din gidan a hankali na shiga_, gabanah sai da ya fad'i saboda gidan ya bala'in haduwa daga gani anarka kud'i a cikinsa, kuma duk Wanda ke zaune a gidan nan ba kara min attajiri bane, juyawan da zanyi sai na hango mutane nata kaiwa da komowa sai kace gidan sarkin Katsina.. Lol, ina karawa gaba sai na ga ashe ma'aikatan gidan ke kaiwa da komowa, kuma na fahimci cewan duka ma'aikatan kowa da bangaren da yake aiki, both of Maza da Matan.

Masu gadin gidan mutum biyu ne, Masu bama flowers ruwa da ban, masu kula da tsaftan tsakar gidan daban, haka zalika masu kula da fanin cikin gidan daban, _na kara shigewa ciki don in bama idona abinci_, na kalla cikin fallon da kyau naga ya hadu sossai colour din fallon red and white nace _woow_ na juya naga dining area shima ya bala'in haduwa, Γ§an kuma sai na hango wata yarinya tana gyara dining din, ta jera wasu had'add'un kuloli, daga gani ba abinci kala daya bane aka dafa ba....

Domin Sauke Cikakken littafin sai ku danna bulun rubutun dake Ζ™asa ko kuma hoton.

πŸ‘‡πŸ‘‡πŸ‘‡πŸ‘‡
https://www.aihausanovels.com.ng/2021/11/hadi-daga-allah-complete-hausa-novel.html
...
*Hajiya Duduwa Mai KanΙ“ari Complete Hausa Novel Document |*

Dandaline cike da "yan mata da samari kidan kalangu na tashi masu rawa nayi masu kallo nayi,sai "babbaka dariya suke.


Gefe guda na hango wata "yar matashiya tana zaune akan wani gungumen itace,sai shan rake take tana susar kai.

Kara matsowa nayi kusa da ita, dariya ce ta kubce mun, ganin irin kwalliyar dake fuskar ta, fuskar tasha panti da wata jar hoda.tayi wasu irin digo_digo a kumatu har zuwa goshinta.

Sannan taja kwalli a kan girarta har kusada kunne ga wani irin jan Jan baki da tasa a saman leben ta kamar zai zube a kasa tsabar yawa.

Tana shan rake abunda hankali kwance tana susar kanta.

Jitayi ana kwala mata kira,HAJIYA DUDUWA ME KAN BARI

hade rai tayi,bata motsa ba tashigaba da shan rakenta ruwan raken duk ya bata mata jiki.

Karasowa budurwar tayi ta tsaya akan ta tace Hajiya duduwa me kan bari, tun daga nesa nake kwala maki kira.kikayi banza dani...

Domin sauke cikakken littafin sai ku danna bulun rubutun dake Ζ™asa ko kuma hoton.


πŸ‘‡πŸ‘‡πŸ‘‡πŸ‘‡
https://www.aihausanovels.com.ng/2021/11/hajiya-duduwa-mai-kanari-complete-hausa.html
...
*Ta Sha Azumi Kuma Babu Damar Da Zata Ciyar*


Shin mace mai cikin da bata samu daman ciyarwa ba a ramadan, yaya za tayi yanzu?

Domin Ganin Amsa sai ku danna bulun rubutun dake Ζ™asa πŸ‘‡πŸ»πŸ‘‡πŸ»πŸ‘‡πŸ»
https://www.aihausanovels.com.ng/2022/03/tasha-azumi-kuma-babu-damar-da-zata.html

PleaseπŸ‘πŸ‘